Translate site

Wednesday 14 October 2015

Twitter zai rage ma'aikata saboda gyare- gyare


Kamfanin Twitter ya ce zai rage guraben ayyuka 336, na ma'aikatansa a wani bangare na sake yin gyare- gyare ga harkokin kasuwancinsa.

Rage guraben ayyukan zai ci tsakanin Dala miliyan 10 da Dala miliyan 20 na kudaden sallama.

Yayinda gyare- gyaren zai ci tsakanin Dala miliyan 5 da kuma Dala miliyan 15 in ji kamfanin Tweeter.

Hannayen jari a Twitter sun tashi zuwa kashi 2% bayan sanarwar.

Wannan mataki na zuwa ne wasu 'yan kwanaki bayan da aka tabbatarwa da Jack Dorsey kujerar babban jami'in gudanarwa na dindindin na Kamfanin.

Ya rike mukamin shugaban kamfanin na rikon kwarya har tsawon watanni uku bayan da Dick Costolo ya sauka a ranar 1 ga watan Yuli.

A wata wasika da ya aike wa ma'aikatan Tweeter, Mr Dorsey ya rubuta cewa: ' Mun dauki shawara mai wahalar gaske-mu na shirin sallamar mutane 336 daga kamfani'.

'Za mu yi hakan ne tare da matukar mutunta kowa' in ji Dorsey

No comments:

Post a Comment