Translate site

Wednesday 2 September 2015

Sojin Nigeria sun kwato Gamboru Ngala

Rundunar sojin Najeriya ta kwace ikon garin Gamboru Ngala, da ke jihar Borno daga hannun mayakan Boko Haram a ranar Talata. A wata sanarwa da rundunar ta fitar, mai magana da yawun rundunar Kanal Sani Usman Kuka-Sheka ya ce yanzu haka dakarun suna ta kokarin tattaro kayan aikinsu da kuma motocin sintiri. Dakarun sojin Najeriyar na cikin murnar wannan galaba da suka samu a kan Boko Haram. A baya sojojin Chadi sun karbo garin a hannun 'yan Boko Haram, amma daga bisani kuma suka sake karbe wa

No comments:

Post a Comment