Translate site

Wednesday 2 September 2015

Mazauna Gamboru sun yaba wa sojin Nigeria

Wasu 'yan asalin garin Gamborun Ngala da ke jihar Borno Najeriya wadanda yanzu ke samun mafaka a wasu wurare sun ce suna murna sosai da nasarar da Allah ya ba wa sojojin Najeriya ta kwato garinsu. Sai dai sun yi kira ga gwamnatin tarayya da ta ba su izinin komawa gidajensu ba tare da bata lokaci ba, suna masu cewa ya kamata gwamnatin ta taimaka musu wajen gyara gidajen da aka lalata musu sakamakon hare-haren Boko Haram. A cewar su, suna cikin mawuyacin hali da suka hada da rashin kudi da rashin sanao'i da abinci. A ranar Talata ne rundunar sojin Najeriya ta ce dakarunta sun kwato garin Gamborun Ngala wanda ke karkashin ikon mayakan kungiyar Boko Haram. Garin yana da matukar muhimmanci ta fuskar kasuwanci, domin kuwa yana hada kasashen Najeriya da Nijar da ma Jamhuriyar Afirka ta Tsakiya.

No comments:

Post a Comment