Translate site

Sunday 13 September 2015

Kamaru: Boko Haram sun kashe mutane


A Kamaru hare-haren 'yan ƙunar baƙin wake sun kashe mutane 10, yayin da wasu da dama suka jikkata a garin Kolofata. Ana kyautata zaton cewa 'yan Boko Haram ne suka kai harin. Wannan dai ba shi ne karon farko da kungiyar Boko Haram ta kai harin garin na Kolofata wanda shi ne mahaifar Mataimakin Firiya Ministan Kamarun Amadou Ali. Bayanai sun ce Gwamnan Lardin arewa mai nisa Mijinyawa Bakary ya je garin na Kolofata domin gane wa idanunsa abin da ya faru. Jiya ma dai an yi bata kashi a tsakanin dakarun tsaro da 'yan kungiyar Boko Haram a garin Balgaram na karamar Hukumar Hile Alifa inda jami'an tsaron suka kashe 'yan kungiyar Boko Haram uku.

No comments:

Post a Comment