Translate site

Tuesday 6 October 2015

Facebook zai samar da intanet a Afirka


Shafin sada zumunta na Facebook zai kaddamar da wani tauraron dan-Adam wanda zai rika samar da intanet a yankunan karkara na Afirka. Mutumin da ya mallaki shafin, Mark Zuckerberg, ya ce za su hada gwiwa da kamfanin tauraron dan-Adam da ke Faransa, Eutelsat, domin kaddamar da shi a watanni shidan farko na shekarar 2016. Mark Zuckerberg ya wallafa a shafinsa na Facebook cewa, "Za mu ci gaba da aiki domin ganin mun samar da intanet a dukkan sassan duniya komai nisan wurin kuwa." Wannan mataki yana cikin shirin Facebook na samar da shafin intanet mai suna Internet.org, wanda ya yi ta shan suka a kasashe da dama. A wasu yankunan kasar Indiya, mutane sun fusata da matakin na Facebook, suna masu cewa hakan zai fifita shi a kan wadanda ke gogayya da shi. Internet.org yana duba hanyoyi daban-daban da zai iya samar da intanet a wurare masu sarkakiya. A kwanakin baya, kamfanin ya ce zai yi amfani da jirage marasa matuka domin samar da intanet a yankuna masu wahalar zuwa.

No comments:

Post a Comment