Translate site

Sunday 13 September 2015

Jam'iyar PDP A JIhar Bauchi Ta kori Shugabanta


Jam'iyar PDP da ta sha kaye a jihar Bauchi ta dauki matakin gyara kura kurai da tace an tafka da ya janyo mata faduwa zabe bara,. Ta kuma sauke wadansu shugabannin jam'iyar tare da barazanar kaisu gaban hukumar EFCC Jam’iyar adawa ta PDP a jihar Bauchin Najeriya ta gudanar da garambawul da ya kai ga tsige shugaban jam’iyar da sakataren jihar, da kuma zaben shugabannin wucin gadi tare da barazanar yiwuwar sa bakin hukumar yaki da cin hanci da rashawa ta kasar EFCC. Mataimakin shugaban jam’iyar kuma dan kwamitin zartaswa Salihu Ya’u Nabardo ya yiwa wakilinmu Abdulwahab Mohammed karin haske dangane da batun.

No comments:

Post a Comment